Skip to main content

MENENE TAMBAYOYIN DA ‘YANMATA SUKE YI??? NA 1


MENENE TAMBAYOYIN DA ‘YANMATA SUKE YI???


ماذا تسأ ل الفتيات؟

NA -1

DAGA

“CIBIYAR NUUN”
MASU WALLAFA DA TARJAMA

FASSARA:

MURTALA ISAH DASS


MUKADDIMA

Akwai tambayoyi (masu yawa) da suke kekkewayawa a cikin rai (kwakwalwar) ko wace budurwa, wadanda take bukatar amsar su, wani lokaci takan koma wajen uwarta ko 'yar'uwarta ko kawarta ko kuma wajen malamarta ta makaranta. Saidai wani lokaci bata gamsuwa da amsar da suke bata. Saboda haka sai kaga son sanin wadannan abubuwan na tunkudata zuwa ga tambayoyi masu dinbin yawa (alhali ta rasa mai bata gamsassun amsoshi)
Yawancin uwaye kunya na lullubesu (suna jin kunya) game da amsa wasu sashen tambayoyi masu tsarkakiya. (Sannan wani bangare kuma ita kanta budurwar ce take jin kunyar yin tambayar alhali abin na damunta tana so ta sami bayani a kan su)
Wannan littafi da ke gaba gareki ya ke 'yar'uwata abar girmamawa, tattararrun tambayoyi ne daga cikin tambayoyi wadanda ake jin kunyar tambayarsu ko kuma in an tambaya ake jin kunyar bada amsarsu.
Hakika "Cibiyar Nuun" mai wallafe-wallafe da fassara, tare da taimakon wasu sashen mata da suka dora wa kansu aikin (taimakon Addinin) musulunci ta hanyar tafiya makarantun (koyar da addinin) musulunci,  da ma wasu makarantun na daban wanda ba na musulunci ba. Sai suka samo (tattaro) wadannan tambayoyi kai tsaye daga 'yanmata kuma dalibai wadanda shekarunsu ya kama daga sha biyu har zuwa karshen matakin makarantar sakandare. Sai wannan cibiya (ta "Nuun") ta kakkasa wadannan tambayoyiyi zuwa maudhu'o'i. Sannan ta bar wasu tambyoyi masu maimaituwa wadanda suka taho ta yanayi mabanbanta, domin samun gamammen amfanuwa.  Kuma hakan sakamakone na cewa wadansu 'yanmata sunyi kebantattun tambayoyi ne wadanda suka saba da tambaya mai kama da su.
Sannan sai muka yi kokarin amsa su ta bangaren kwararru game da sanin zamantakewar hadakar jama'a. Sannan a daya bangaren kuma sai daya daga cikin manyan shehunan malaman mu na Hauzar ilimi ya kawo bayanin hukuncin shari'a a bisa ko wace tambaya.
Daga karshe muna mika godiya ga dukkan wadanda ke da kaso na taimakawa wajen fiddo da wannan littafi zuwa samuwar sa. Muna masu rokon Allah Mai tsarki da daukaka da Ya karba musu wannan aiki da suka yi domin Sa. Kuma da fatar wannan kokari ya amfanar da 'yanmatan mu da uwayen mu da malaman mu mata, domin warware matsaloli masu yawa wadanda suke kunshe a kwakwalen su (wadanda suka kasa samun amsoshin da zai warkar da su).
Sannan muna fata al'uma zasu kasance tare da mu wajen saduwa da mu ta yanda idan akwai wasu tambayoyi wadanda (ke kwakwalen su amma) basu samesu ba a cikin wannan littafi. Muna sanar da su cewa mun shirya tsaf domin amsa su a cikin sabon bugu mai fitowa ko a littafi mai biye wa wannan, in Allah Madaukaki Ya so.
Daga:Cibiyar Nuun” domin wallafa da tarjama.





























KASHI NA FARKO
DORUWAR AYYUKAN SHARI'A (TAKLIFI) A WAJEN BUDURWA.
Tambaya ta 1-
Yaushe ne ya wajaba a kan budurwa ta aikata wajiban shari'a?

Amsa:
 Yana wajaba ne ga budurwa ta aikata wajibanta na shari'a a yayin da ta isa wacce taklifi ya hau kanta a shara'ance. Kuma wannan taklifi yana tabbata ne a kan ta a yayin da sharuda guda uku suka tabbatu a kanta
Na farko;  Balaga. Kuma shi (balaga) yakan tabbata ne aka budurwa da cikan shekaru tara na watannin kamariyya (kirgen watannin musulunci)
Na biyu: Hankali. Babu taklifi a kan mahaukaciya. Sannan hankali a nan yana nufin ikon banbance abu maikyau da mummuna (kenan ko da yarinya ta kai shekara tara amma tana da wauta ta yanda bata iya banbance abu maikyau da mummuna to taklifi ba zai hau kan ta ba)
Na uku: Ikon aikata aiki. Bai wajaba ga budurwa ta aikata abinta take da gajiyawa wajen aikatawa ba (kamar in ba zata iya daukar azumi ba)





Tambaya ta 2-
Shin ba za'a iya daukan dora taklifin wajabcin aikata shari'a akan budurwa a wadannan shekaru (tara) al'amari ne wanda ya fi karfin ikonta a bisa tsayuwa akan wadannan wajibai na ibada ba?

Amsa:
Lallai shari'ar musulunci mai daraja tare da doruwar aikata hukun-hukunce (taklifi) a cikinta ya tattaru ne tare da ikon budurwa a shekarunta na balaga. Koda yake budurwa tana iya gazawa wani lokaci wajen iya gudanar da wasu sashen ayyukan ibada na wajibi kamar azumi a bisa misali. A nan sai hukuncin wajabcin azumin ya sauka a kan ta a watan ramadhana din, sai ta rama shi kafin wani watan ramadhana mai zuwa (a lokacin ta kara girma da samun ikon iya yin azumin). Idan kuwa (duk da hakan) ta gajiya (ta kasa aikatawa) to wajabcin yin azumin ya sauka a kan ta gaba daya. Anan sai ta wadatu da biyan fansa, wanda shine ciyar da miskini guda daya ko wace rana kilogram uku. Idan tayi hakan to babu wajabcin ramuwa a wasu shekaru masu zuwa koda tana da ikon yin hakan.
Ya ke 'yar'uwa ta abin girmamawa,  ya kamata ki san cewa Allah Madaukakin sarki bai kallafa wani abu a kanki ba face kina da ikon aikata shi.  Sallah da azumi da khumusi da hajji da sadaka da rikon amana da barin (haramta) yi da wani da annamimanci da sata da makamantan su dukkansu abubuwa ne na al'ada ga ko wani mukallifi (zai iya aikata wadanda ake bukatar ya aikata da barin wadanda aka hana shi aikatawa). Idan kuwa  gazawa ta bijiro to babu wannan taklifi a kan sa.
Allah Madaukakin sarki Ya fada "Allah baya kallafa wa wata rai bace iyawarta" (Bakara, aya ta 286)
"Ba Mu kallafa wa wata rai face iyawarta" (An'am,  aya ta 152)

Tambaya ta 3-
Me ya sa lokacin balaga ya kan tabbata ga budurwa gabannin saurayi? Shin haka yana da alaka da doruwar ayyukan shari'a?

Amsa:
Allah Mai tsarki da daukaka Ya halicci na miji da mace,  kuma sai ya sanya kebantattun abubuwa da bambance-bambance a cikin halittarsu ta jiki da rai. Ko wani dayansu na cike na dayansa. Bai sanya su masu kama da juna ba, saboda kamanceceniyarsu zai kore (hana) cikar (gina)  hadakar zamantakewa. Lokacin balaga a wajen budurwa yakan rigayi lokacin balagar saurayi. Wannan yana faruwa ne sakamakon abinda mace ta kebanta da shi wanda ba a samu a wajen saurayi. Saboda haka a lokacin da ta kai shekarun balaga sai ta sami daukaka da dora mata hakkokin shari'a (taklifi). To sai a wannan lokaci sai aikata ayyukanta na shari'a su wajaba a kanta. Wannan kuma ba yana jayo mata tawaya bane, saidai ma balagar a gareta daukaka ce da girmamawa.
'Yar'uwa ta abin girmamawa,  kada ki kwatanta lokacin taklifin ki da na wani. Ke dai ki yi tunanin yanda zaki tabbatar da kamalarki da samun kyakkyawar rayuwar lahira. Ki fadaka da cewa za a tashe ki (daga kabari bayan mutuwar ki)  ke kadai ne,  kuma hisabin ki ma ke kadai za'a miki (game da abubuwan da kika aikata). Saboda haka ke dai ki yi kokarin tsarkake ayyukan ki ga Allah Madaukaki. Ki yi aiki domim kubutar da kanki. Allah Madaukaki Yana fada a cikin Suratul Zalzala "A ranar nan ne mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu"

Tambaya ta 4-
Wadansu suna daukar cewa dora nauyin shari'a ga budurwa a wadannan shekaru yana nuna tamkar zaunci ne gare ta, wani lokaci ma suna ganin cewa hakan tawaya ce gareta. Shin za ku iya bayyana mana hakikanin yanayi ko matsayin wannan taklifi?

Amsa:
Allah Madaukaki Ya halicci mutum sai Ya sanya masa ayyukan shari'a wanda wadannan ka'idodi na shari'a suna kaiwan sa ne zuwa ga daukakar sa (kamalar sa) da samun arzikin sa na lahira. Kuma wadannan shari'o'i suna kunshi wajibai da muharramai (abubuwan da ya wajaba a aikata da kuma wadanda suke haramun ne aikata su). Kuma dukkan ayyuka na wajibi akwai amfanuwar mukallifin a cikinsu, kuma dukkan abinda aka haramta akwan barna ne gare shi. To a yayin da mutum ya zama balagagge, mai hankal,i mai ikon aikatawa, sai ya zamo an kallafa masa wadannan ayyuka na shari'a, amma ba wani abu bane mai nauyi wanda aka dora masa.
'Yar'uwata abar girmamawa, ya kamata ki san cewa lallai Allah Mai girma da daukaka bai wajabta wani abu a kan ki ba face akwai maslaha gareki, haka nan bai haramta wani abu akan ki ba face akwai barna (matsala)  a cikinsa. To idan kika aikata wajibai kuma ki ka bar aikata muharramai,  a nan kin kasance mai tabbatar da da amfani ga kanki ne, kuma kin nisantar da kan ka ga barna ne. To kin ga haka kuwa alheri ne da daukaka (kika jawo wa kan ki). Hakan sam-sam ba zalunci da tawaya ba ne. Ki kara fahimtar cewa shi taklifi (doruwan zartas da shari'a akan mutum) daukaka ne da girmamawa. Saboda haka isar ki lokacin balaga kafin na saurayi (namiji) wannan na nuni ne ga cewa  ke kin shiga duniyar wadanda Allah Ya daukaka su a gabannin sa. (Kenan hakan fifiko ne a kansa wanda ya kamata ki yi alfahari da shi, amma ba daukar hakan a matsayin zalunci da tawaya ba)

Tambaya ta 5-
Don me Allah Madaukaki Ya sanya bukata a cikin ran mu? Kuma don me wasu sashen wadannan bukata suna tahowa ne a shekarun balaga?

Amsa:
Allah madaukakin sarki Ya halicci mutum ne daga (bangarori biyu na) ruhi da jiki. Sannan sai ya cusa wasu tarin lamura na neman biyan bukata. Wasu (bukatar) sukan tunkuda mutun wajen cin abinci, ko shan abin sha, ko bukatuwar numfashi da sauran bukatu. Kuma da wdannan al'amura ne kiyaye jiki yake samuwa. To amma wasu bangaren bukatar sukan auku ne a lokacin da aka kai matakin balaga (a yayin da mace za ta iya jin bukata ga namiji, haka shima na miji zai ji bukatar mace). Manufar wannan bukata na lokacin balaga kuwa ci gaba ne na samar da nau'in dan-adam, idan babu wannan bukata ba za'a sami aukuwar aure ba, idan kuwa ba'a yin aure ba za'a sami haihuwa ba, kenan zai zamo babu ci gaban samuwar mutum a bayan kasa, haka kuma zai haifar da yankewa zuriyar mutum. Saboda haka sai ya zamo samuwar wannan bukata wajibi ne domin cigabantar da samuwar mutane.
'Yar'uwata abar girmamawa, ina miki horo da cewa ki bi hanyar gaskiya, ki yi mu'amala da bukatar ki ta hanyar tsayuwa bisa iyakokin da shari'ar (addinin)musulunci ya iyakance. Kada ki bi son rai da shedan. Domin bin son rai da batarwar shedan yana bata budurwa,  kamar yanda bacin budurwa kaso ne na abinda ke bata hadakar zamantakewar al'uma. Kuma ranar tashin kiyama yana zamowa azaba ne mai tsanani.

Tambaya ta 6-
Ban san menene alhakin da ya hau kaina na shari'a ba a matakin balaga ta, kuma ina jin kunyar in yi tambaya a kan haka. To mene ne ya hau kai na in yi?

Amsa:
Ya wajaba akan ko wani mutumin da ya isa matakin taklifi ya nemi sanin wajibobin da ke kan sa domin ya aikata su. Sannan haka ma ya nemi sanin abubuwan da suka haramta a kansa domin ya bar su kuma ya nisance su. To a nan akwai hanyoyi masu yawa wanda mukallifi zai bi wajen sanin abubuwan da suka doru a kansa na shari'a. Daga cikin su akwai;
Ø Tambayar uwa
Ø Tambayar kwararru wajen sha'anin tarbiyyar addini a makarantu
Ø Kwararru akan halittar mata, da masu irshadi ga mata.
Ø Kuma zai iya yiwuwa a tambayi malami masanin addini ko da ta hanyar tarho ne. Da makamantan su.
Kuma ya kamata dukkan jama'a su san cewa wasu sashen al'amuran addini ya kamata ga mutum mumini ya yi tambaya game da alhakin da ya doru a kan sa game da su, ko da kuwa tambayar za ta jawo jin kunya. Domin sanin hukunce-hukuncen shara'a shine abu mafi muhimmanci daga komai a cikin rayuwar mu.

Wa sallallaahu alaa Muhammad wa alaa aalihit taahiriin.


Kashi na biyu zai amsa tambayoyin da ya shafi alaka tsakanin na miji da mace, ko alaka tsakanin saurayi da budurwa.

A biyo ni da izinin Allah.

























Murtala Isah Dass
(8 RABI’US THANI, 1439 / 27 DECEMBER, 2017)
Domin neman Karin bayani/ Gyara ko Kalu-bale, a tuntubeni ta daya daga cikin wadannan lambobi;
08133289306,  08058636125 & 07083030309.
Haka ma za a iya saduwa da ni ta Whatsapp a wannan lambar; 08058636125
Ko a sadu da ni ta daya daga cikin wadannan Adireshin Email:
Sannan ana iya samun wannan kasida da wasu makamantan sa a wannan website na internet:

Comments

Popular posts from this blog

SHIN GASKIYA NE ‘YAN SHI’A SUNA TUHUMAR UMMUL MUMININA A’ISHA DA AIKATA ZINA?

SHIN GASKIYA NE ‘YAN SHI’A SUNA TUHUMAR UMMUL MUMININA A’ISHA DA AIKATA ZINA? Daya daga cikin abinda makiya shia suka dau tsawon zamani suke yadawa na karya akan ‘yan shia domin kyamatar da al’uma da wannan mazhaba ta ‘ya’yan gidan Manzon tsira s.a.w.a shine cewa wai suna da kudurin dora wa Matar Manzo A’isha ‘yar khalifa Abubakar tuhumar aikata zina (wal’iyazu billah). Da alama wadanda suka tsara wannan qaryar basu san cewa wata rana duniya za ta iya kasancewa tamka gari guda ba ta tayanda babu abinda zai buya ga wani. Yanzu dai ga ‘yan shia ko ina ana tare da su, ga malaman su cikin sauki za’a iya tuntuban su sannan ga dubban litattafan su a kasuwa kowa na iya saye ya karanta, uwa uba kuma ga yanar gizo wanda cikin lokaci kankani mutum zai binciki irin littafin da kake bukata ya karanta. Wani abin mamaki shine sai ga ‘yan shia basu ma yarda da wannan tuhumar akan ita Ummul muminina A’isha ba balle kuma tabbatar da tukuhumar a kan ta. Za mu duba bayanan malaman shia game da wannan a...

AUREN MUTU'A TSAKANIN MUSULMI

AUREN MUTU'A TSAKANIN MUSULMI (1) Sheikh Sale Sani Zaria Idan mutum ya bibiyi abubuwan da ake fada da rubutawa a kan Auren Mutu’a a wannan zamani daga malaman Ahlus Sunna. A dukkanin abubuwan da ake fada akwai abubuwa masu jan hankali matuka wanda ake bukatar al'umar musulmi su fahimci hakikanin sa. Alhamdu lillahi dukda cewa su malaman suna kokarin fada da wannan ibada amma anyi dace suka yarda da halaccin Mutu ’ a da ayar AlKur ’ ani ta cikin Surar Nisa ’ i aya ta 24. A kan haka ne ma nake ganin cewa duk mai hankali zai yi mamakin yadda wasu malamai suke kwatatnta auren mutu ’ a da "dadiro" ko "kwanan gida". Idan har mutum ya yarda da cewa akwai ayar AlKur ’ ani wadda ta halatta Mutu’a ko da kuwa ya yarda da cewa an goge ta daga baya, to da wace irin mahanga kuma yake kwatanta shi da dadiro da kwanan-gida? Ina ayar da ta taba halatta dadiro da kwanan-gida a AlKur ’ ani har ya cancanci irin wannan kwatanci? Dadiro fa alfasha ne! Yanzu yana jin cewa ...